Daga: Abdulrazak Ahmad Jibia
Mataimakin shugaban majalissar malamai ta kungiyar Izala dake tarayyar najeriya Sheikh Barr. Ibrahim Sabi'u Jibia ya yi kira ga 'yan kasuwa dasu saukaka farahin kowane irin nau'in kaya musamman a cikin watan azumin ramadana.
Ya ce ana bukatar kowane musulmi yayi koyi da shugaban halittu Annabi Muhammad (S.A.W) wajen yawaita taimako da bada tallafi ga Marayu, Gajiyayyu, da sauran mabukata, domin a cikin watan azumi ne Allah ke gafartawa bayinsa.
Ya kara da cewa yana da kyau 'yan kasuwanmu su kara saukaka farashi hatta wandanda ba musulmai ba su amfanu da romon azumin watan ramadana, saboda manzom tsira (A.S) ya kasance mai fadada kyauta a acikin watan azumi duk da cewa shi mutum ne mai yawan kyauta a koda yaushe.
Sannan ya yi kira ga masu rike da mukami na siyasa dana sarauta gami da attajirai cewa suji tsoron Allah su jajirce wajen taimakawa na kasa dasu domin karfin da Allah yayi masu.
Kazalika suma talakawa ba'a barsu a baya ba, yana da kyau suma suyi sadaka daidai kwargwadon abinda Allah ya hore masu koda kwayar dabino ne.
Daga karshe ya bayyana cewa a cikin watan azumi ne ake daure dukkanin sheidanu masu tauye bayi daga bautar Ubangijinsu, to saboda haka yana da kyau a cikin watan azumi mu sakankance masu bautawa Ubangijin fiye da kowane lokaci.
Shehin malamin ya yi wannan kira ne makon daya gabata a harabar gidansa dake unguwar sarki kusa da fadar mai girma sarkin arewan Katsina, hakimin Jibia.
Muna rokon Allah madaukakin sarki ya kawo mana rangwame, kuma ya bamu ikon yin amfani da wannan nasiha Amin.
Mataimakin shugaban majalissar malamai ta kungiyar Izala dake tarayyar najeriya Sheikh Barr. Ibrahim Sabi'u Jibia ya yi kira ga 'yan kasuwa dasu saukaka farahin kowane irin nau'in kaya musamman a cikin watan azumin ramadana.
Ya ce ana bukatar kowane musulmi yayi koyi da shugaban halittu Annabi Muhammad (S.A.W) wajen yawaita taimako da bada tallafi ga Marayu, Gajiyayyu, da sauran mabukata, domin a cikin watan azumi ne Allah ke gafartawa bayinsa.
Ya kara da cewa yana da kyau 'yan kasuwanmu su kara saukaka farashi hatta wandanda ba musulmai ba su amfanu da romon azumin watan ramadana, saboda manzom tsira (A.S) ya kasance mai fadada kyauta a acikin watan azumi duk da cewa shi mutum ne mai yawan kyauta a koda yaushe.
Sannan ya yi kira ga masu rike da mukami na siyasa dana sarauta gami da attajirai cewa suji tsoron Allah su jajirce wajen taimakawa na kasa dasu domin karfin da Allah yayi masu.
Kazalika suma talakawa ba'a barsu a baya ba, yana da kyau suma suyi sadaka daidai kwargwadon abinda Allah ya hore masu koda kwayar dabino ne.
Daga karshe ya bayyana cewa a cikin watan azumi ne ake daure dukkanin sheidanu masu tauye bayi daga bautar Ubangijinsu, to saboda haka yana da kyau a cikin watan azumi mu sakankance masu bautawa Ubangijin fiye da kowane lokaci.
Shehin malamin ya yi wannan kira ne makon daya gabata a harabar gidansa dake unguwar sarki kusa da fadar mai girma sarkin arewan Katsina, hakimin Jibia.
Muna rokon Allah madaukakin sarki ya kawo mana rangwame, kuma ya bamu ikon yin amfani da wannan nasiha Amin.
Comments