Mataimakin Shugaban Majalissar Malamai ta kungiyar JIBWIS dake tarayyar najerya, Sheikh Barr. Ibrahim Sabi'u "Sarkin Malaman Jibia", ya ja hankullan 'yan uwa musulmi da subi umarnin shugabbani madamar bai saba wa addinin musluncii ba.
Ya ce bai kamata talakawa/mabiya suyi jayayya da abinda hukuma tayi umarni a matsayin maslaha ga al'umma ba.
Ina jawo hankulla musamman na 'yan uwa Malamai da Almajirai cewa ita tafiya ta addinin muslunci dole sai anyi biyayya ga Allah da Manzonsa da kuma hukuma, da abinda yake maslaha ga al'umma.
Idan aka umarcemu da aikata wani abu ko kaurace masa, to kada ya zamo matsala, saboda duk abinda aka ce kada ayi a wannan yanayin magana ce dake nuna ba'a bukatar taron jama'a a wurin.
Maganar sallar juma'a da aka a dakatar da yinta a masallamatan juma'a ba matsala bane saboda babu Wanda aka hana yaje gida yayi.
Saboda haka ina kara jawo hankullan 'yan uwa na Almajirai cewa kada mutum ya dauka idan yayi karatu "ya zama malamin komai; dole ne akwai abinda bakai za a tambaya ba sai wanda yayi karatu a fannin.
Duba da halin da muke ciki na cutar korona (Covid-19), ina kira ga mutane a fannin lafiya abar wa malaman lafiya aikinsu, saboda daga gare sune gwamnatoci ke karbar fatawoyi kan yadda za a kawo karshen yaduwar wannan cuta da kuma kare rayukan al'umma da kamuwa da ita.
Yana da kyau kowa ya tsaya bakin iliminsa, kada malami ya dauka cewa idan aka saka doka banda shi, domin karatu daban kuma bin doka ma daba.
Wajibi ne ga malamai subi doka kamar yadda kowa yake bin ta, hasalima su ake kyautatawa zaton cewa sune masana doka kuma su suka san darajar masu doka, saboda haka ya kamata malamai su bita fiye da kowa.
Sannan kada malamai su biyewa mazuga, su afka ga fitina, idan ance ayi abu kaza " AYI" idan kuma akayi hani to "A BARI. Mun sani babu wanda za ace kada yayi sallah.
Dakatar da yin Sallar Juma'ar nan fa da ace mutane sun wayi gari ana ruwan sama har lokacin sallar yayi, da mutune ba zasu ce dole sai sunje masallaci ba a gida ma za su iya tsayawa suyi sallar azhur. Kamar yadda matafiyi zai ga ana sallar juma'a akan hanyarsa ta zuwa wani gari ba zai yita ba har sai idan ya isa gida shima yayi sallar azhur.
Daga karshe ina nasiha a garemu, masu zuga wasu don Allah su daina, da fatan Allah ya kawo mana karshen wannan Annoba Amin.
****
Shehin malamim ya isar da wannan sako ne akan mimbari yayin khudbar sallar Juma'a.
Danna wannan LINK din dake kasa domin sauke AUDIO akan wayoyinku
👇👇👇👇👇
https://web.darulfikr.com/s/87402
Ku cigaba da kasancewa damu a shafukanmu na yanar gizo👇
Website:
www.masisjanigeria.blogspot.com
Email:
masisjanigeria@gmail.com
Whatsapp:
https://wa.me/2347044677956
_________________
Masisja Nigeria
17/04/2020
Ya ce bai kamata talakawa/mabiya suyi jayayya da abinda hukuma tayi umarni a matsayin maslaha ga al'umma ba.
Ina jawo hankulla musamman na 'yan uwa Malamai da Almajirai cewa ita tafiya ta addinin muslunci dole sai anyi biyayya ga Allah da Manzonsa da kuma hukuma, da abinda yake maslaha ga al'umma.
Idan aka umarcemu da aikata wani abu ko kaurace masa, to kada ya zamo matsala, saboda duk abinda aka ce kada ayi a wannan yanayin magana ce dake nuna ba'a bukatar taron jama'a a wurin.
Maganar sallar juma'a da aka a dakatar da yinta a masallamatan juma'a ba matsala bane saboda babu Wanda aka hana yaje gida yayi.
Saboda haka ina kara jawo hankullan 'yan uwa na Almajirai cewa kada mutum ya dauka idan yayi karatu "ya zama malamin komai; dole ne akwai abinda bakai za a tambaya ba sai wanda yayi karatu a fannin.
Duba da halin da muke ciki na cutar korona (Covid-19), ina kira ga mutane a fannin lafiya abar wa malaman lafiya aikinsu, saboda daga gare sune gwamnatoci ke karbar fatawoyi kan yadda za a kawo karshen yaduwar wannan cuta da kuma kare rayukan al'umma da kamuwa da ita.
Yana da kyau kowa ya tsaya bakin iliminsa, kada malami ya dauka cewa idan aka saka doka banda shi, domin karatu daban kuma bin doka ma daba.
Wajibi ne ga malamai subi doka kamar yadda kowa yake bin ta, hasalima su ake kyautatawa zaton cewa sune masana doka kuma su suka san darajar masu doka, saboda haka ya kamata malamai su bita fiye da kowa.
Sannan kada malamai su biyewa mazuga, su afka ga fitina, idan ance ayi abu kaza " AYI" idan kuma akayi hani to "A BARI. Mun sani babu wanda za ace kada yayi sallah.
Dakatar da yin Sallar Juma'ar nan fa da ace mutane sun wayi gari ana ruwan sama har lokacin sallar yayi, da mutune ba zasu ce dole sai sunje masallaci ba a gida ma za su iya tsayawa suyi sallar azhur. Kamar yadda matafiyi zai ga ana sallar juma'a akan hanyarsa ta zuwa wani gari ba zai yita ba har sai idan ya isa gida shima yayi sallar azhur.
Daga karshe ina nasiha a garemu, masu zuga wasu don Allah su daina, da fatan Allah ya kawo mana karshen wannan Annoba Amin.
****
Shehin malamim ya isar da wannan sako ne akan mimbari yayin khudbar sallar Juma'a.
Danna wannan LINK din dake kasa domin sauke AUDIO akan wayoyinku
👇👇👇👇👇
https://web.darulfikr.com/s/87402
Ku cigaba da kasancewa damu a shafukanmu na yanar gizo👇
Website:
www.masisjanigeria.blogspot.com
Email:
masisjanigeria@gmail.com
Whatsapp:
https://wa.me/2347044677956
_________________
Masisja Nigeria
17/04/2020

Comments