Skip to main content

MA'ANAR SHI'A DA MANUFOFINSU (003)

Wannan raddi ne na uku zuwa ga Ado Lamama game da shirmenda yayi a matsayin raddi zuwa ga Malamin sunnah Alkali Sheikh Lawal Musa Jibia.
Daga: Sheikh Mustafa Mansur Jibia

Ado  ya ce: Saed bn musayyib shima dan shia ne kuma shine shugaban masu tafsiri na tabi'ai.

To ni kuma nace sam ba dan shia ba NE kuma ma karya ce shi ba malamin tafsiri ba NE,  ko da yake shi lamama bai fadi madogararsa ba, amma ni ku biyo ni ku ga tawa madogarar.

 Saed bn musayyib dai haifaffen garin madina NE,  kuma tabi'i NE,  daya ne daga cikin maruwaita hadisin manzon Allah,  kuma daya daga cikin masana fiqhun madina guda bakwai daga cikin tabi'ai, anayi masa laqabi da babban malamin madina kuma shugaban tabi'ai. Idan mai karatu dalibin ilmi ne ko nan na tsaya zai fahinci lalle Saed bn musayyib sunni NE,  saboda kasancewarsa mutumin madina kuma mahaifinsa sahabi haka ma Kakansa.

Bugu da kari acikin madina ne Ya kare rayuwarsa.

Ga sahabbanda yayi karatu a wurinsu: zaid bn thabit, saad bn abi waqqas, Abdullahi bn Abbas, Abdullahi bn Umar, Nana Aisha, ummu Salamah, Aliyu bn Abi dalib, Suhaibu Rumiy, Muhammad bn Maslamah, Abu Hureira sai Umar bn khattab. Saed bn musayyib saboda shakuwarsa da Abu Hureira har diyarsa ya aura, wanda Wannan ya basa damar kwankwadar ilmin hadisi a wurin sirikinsa.

Duk wannan bayanan nawa ba nina kagesu ba  Imamu Zahabi ne Ya fadesu  a littafinsa na siyaru aalamin nubalaa.

 Sannan mai wahbatuz zahiyliy ga abinda yake Cewa akan salon binciken fiqh na Saed bn musayyib :إعتمد سعيد بن المسيب في منهجه الفقهي على القرآن والسنة والاجماع والقياس فإن لم يجد حكما تخير من أقوال الصحابة. 

Ma'ana Saed bn musayyib Ya dogara ne a wurin tsarinsa na fiddo hukuncin fiqhu akan Alkur'ani da sunnah da Ijmai da kuma Qiyasi.

To naji dan shine zai kafa hujja da Sunnah?  Sannan kuma Imamu zahabiy a dabaqatul kubrah ga abinda yace kan Saed bn musayyib :كما امتاز سعيد بن المسيب بميزة القدرة في تعبير الرؤى ألتي اكتسبها من اسماء بنت ابي بكر الصديق ألتي أخذتها عن ابيها. 

Ma'ana kamar yadda Saed bn musayyib Ya fifita da fifikon iko kan fassarar mafarki Wanda Ya koya daga Asmau bintu Abubakar Wanda ita ma ta koya daga babanta.

Jamaa ku gane mani hanya! Dan Shi'a zai je gidan sayyidnah Abubakar neman ilmi?

 Daga karshe don kada in tsawaita, karya mai lamama keyi da yace Saed bn musayyib shine shugaban masu tafsir na tabi'ai, amma ga maganar imamu zahaby ورغم علمه بالحديث النبي الا ان سعيد بن المسيب كان يعرف عن تفسير القرآن كما كان يحب الشعر وكان لا ينشده.  Maana duk da dinbin ilminsa na hadisin Annabi sai dai Saed bn musayyib Ya kasance yana dari dari da tafsirin Alkur'ani kamar yadda yana sauraron wake amma shi baya rerawa.

Da yan wadannan kalmomin ne nike fahimtar Saed bn musayyib Sunni ne ba shia ba, duba da an haifeshi ne run duniya na cikin hayyacinta hijra shekara 15 kuma Ya rasu a shekara ta 95. سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت أستغفرك وأتوب إليك

MASISJA NIGERIA 
31/05/2020

Comments

Popular posts from this blog

Makarantar Sheikh Ibrahim Sabi'u Jibia ta gudanar da taro domin sanin makamar aiki

Makarantar Sheikh Ibrahim Sabi'u Jibia (MASISIJA) ta gudanar da muhimmin taro domin sanin makamar aikinta na yada da'awar maluman muslunci.  Ranar laraba 10/06/2020 wasu daga cikin jagororin wannan kungiya suka yi taro inda suka tattauna akan muhimman abubuwanda zasu taimaka masu a fagen aikinsu.  Watanni biyu da suka gabata kungiyar MASISJA ta shirya wata muhadara mai taken "Tambayoyi da Amsoshi" ta tsawon sati shidda (6) wadda Sheikh Barista Ibrahim Sabi'u Jibia ke gabatarwa.  A cikin ikon Allah,  an gabatar da ta tsawon makonni hudu (4) sai cutar Covid-19 ta billo wanda hakan yasa hukuma ta dakatar da dukkanin wani taro domin samun kariya daga cutar.  To Allah da ikonsa kuma bayan cutar ta lafa a jihar Katsina, yanzu an cigaba da harakoki kamar yadda aka saba.  Saboda haka ne kungiyar MASISJA, a karkashin wannan mitin, ta shirya tsaf domin cigaba da muhadarar tsawon sati biyu wadda mata ne kadai za ayi wa banda maza ka...

MA'ANAR SHI'A DA MANUFOFINSU (001)

Wannan raddi ne zuwa ga Ado Lamama game da shirmenda yayi a matsayin raddi zuwa ga Malamin Sunnah Alkali Sheikh Lawal Musa Jibia.  Daga: Sheikh Mustafa Mansur Jibia Da farko Inaso in fara da bayani akan minene shia.  Hakika shi'a kishiyar sunnah ce ta fuskar akida.  Sunnah tana nufin addinin da manzon Allah Ya zo dashi kuma mai yin irinsa ya yarda da sahihancin sayyidnah Abubakar, umar, Uthman da Aliyu, tareda gamsuwa da tsarkin dukkanin matayen manzon Allah, gami da yarda da cewa duk sahabbai adalai NE. To wannan shine atakaice maganar Sunnah, kuma kishiyar hakan to shine shia, kamar kudurce cewa sayyidnah Abubakar, umar da uthman mutanen banza ne kuma yan wuta, sannan matan manzon akwai na banza acikinsu, musamman Nana Aisha Da Nana Hafsah sannan hadi da kafirta wani adadi na sahabban manzon Allah. To idan masu sauraro Sun fahinci banbance babancen to akan hakane zan gina raddi na akan rubutun da akayi.  Don haka a biyo don ...

Ya kamata a dinga tabbatar da sahihancin labari kafin a yada - Sheikh Sabi'u Jibia

Sheikh Ibrahim Sabi'u ya yi kira ga 'yan Social Media da su dinga tabbatar da Ingancin labari kafin su yada shi. Mataimakin shugaban majalissar ta kungiyar JIBWIS dake tarayyar najeriya Sheikh (Barr) Ibrahim Sabi'u Jibia, a yayin da yake gabatar da khudbar sallar juma'a yayi kira  ga masu amfani da kafafen sadarwar zamani (Social Media) su guji yada sharri da labarin karya. Ya kara da cewa: yana da kyau mutane  su dinga bincike domin tabbar da ingancin labari kafin su yada shi don gudun aikata abinda zai sa mutum ya wayi gari yana mai ladama game da abinda ya aikata. Kazalika ya karanto ayoyi daga  alqur'ani mai girma da hadisan Annabi (S.A.W) wadanda suke magana akan haramcin yin irin wannan mummunan aiki, wanda yin haka babban abin kyama ne a wajen Allah madaukakin sarki. A cewarsa tsawon lokaci da ya gabata akan samu batagarin malamai ne masu karantar da hadisan karya a yayin da suke karantar da dalibansu, amma yanzu zamani ya canza, kana kwance a gida za kai ta ...