Skip to main content

[RASHIN TSARO]: Sakon Jaje Game da Iftala'in 'Yan Ta'addan Jihar Katsina~Barista Ibrahim Sabi'u

Sheikh Barista Ibrahim Sabi'u Jibia, tsohon sakataren shari'a na jihar Katsina, ya jajantawa al'ummar jihar a bisa iftala'in 'yan bindiga,  barayin dabbobi, dake addabarsu ba dare ba rana.

Sanin kowane cewa tuntuni wadannan batagari suke kai hare-hare a bangarori daban-daban na jihar, musamman a yankunan Batsari, Kankara,  Dan-musa da sauransu. 

Ya kara da cewa hatta ranar laraba 6 gawatan mayun shekara ta 2020, labari ya zo masu inda aka shaida masu cewa yan ta'addar sun shiga kauyen zandam dake karamar hukumar Jibia. Wanda wani lokaci daya gabata ma sun taba shiga garin inda suka jikkita wasu, suka tafi da dabbobinsu.

Barista Sabi'u Jibia yayi kira ga Al'ummar kan su dukufa dayin addu'o'i a cikin wannan wata na ramadana, a lokacin sahur da lokacin shan ruwa, da kuma lokacin da ake sallah musamman a cikin sujjada. Ya ce kada a gajiya, domin addu'ar mu'umini bata faduwa kasa.

Tsohon Sakataren Shari'ar Ya yi kira ga Gwamnatoci da suji tsoron Allah! 

Ya ce tabbas 'yan ta'addar nan basu fi kafin gwamnati ba, saboda akwai wasu munafukai a cikinsu wadanda dasu ake hada kai ana wannan ta'addancin. 

Daga karshe malamin yayi addu'ar nemawa Al'ummar zaman lafiya, tare da addu'ar nema masu sakayyar Allah akan zaluncin da ake yi masu. 

Muna addu'a Allah ya kawo mana zaman lafiya Amin.

*****
Danna wannan LINK din dake a kasa domin sauke sautin wayoyinku👇

AYI SAURARO LAFIYA

Comments

Popular posts from this blog

Makarantar Sheikh Ibrahim Sabi'u Jibia ta gudanar da taro domin sanin makamar aiki

Makarantar Sheikh Ibrahim Sabi'u Jibia (MASISIJA) ta gudanar da muhimmin taro domin sanin makamar aikinta na yada da'awar maluman muslunci.  Ranar laraba 10/06/2020 wasu daga cikin jagororin wannan kungiya suka yi taro inda suka tattauna akan muhimman abubuwanda zasu taimaka masu a fagen aikinsu.  Watanni biyu da suka gabata kungiyar MASISJA ta shirya wata muhadara mai taken "Tambayoyi da Amsoshi" ta tsawon sati shidda (6) wadda Sheikh Barista Ibrahim Sabi'u Jibia ke gabatarwa.  A cikin ikon Allah,  an gabatar da ta tsawon makonni hudu (4) sai cutar Covid-19 ta billo wanda hakan yasa hukuma ta dakatar da dukkanin wani taro domin samun kariya daga cutar.  To Allah da ikonsa kuma bayan cutar ta lafa a jihar Katsina, yanzu an cigaba da harakoki kamar yadda aka saba.  Saboda haka ne kungiyar MASISJA, a karkashin wannan mitin, ta shirya tsaf domin cigaba da muhadarar tsawon sati biyu wadda mata ne kadai za ayi wa banda maza ka...

MA'ANAR SHI'A DA MANUFOFINSU (001)

Wannan raddi ne zuwa ga Ado Lamama game da shirmenda yayi a matsayin raddi zuwa ga Malamin Sunnah Alkali Sheikh Lawal Musa Jibia.  Daga: Sheikh Mustafa Mansur Jibia Da farko Inaso in fara da bayani akan minene shia.  Hakika shi'a kishiyar sunnah ce ta fuskar akida.  Sunnah tana nufin addinin da manzon Allah Ya zo dashi kuma mai yin irinsa ya yarda da sahihancin sayyidnah Abubakar, umar, Uthman da Aliyu, tareda gamsuwa da tsarkin dukkanin matayen manzon Allah, gami da yarda da cewa duk sahabbai adalai NE. To wannan shine atakaice maganar Sunnah, kuma kishiyar hakan to shine shia, kamar kudurce cewa sayyidnah Abubakar, umar da uthman mutanen banza ne kuma yan wuta, sannan matan manzon akwai na banza acikinsu, musamman Nana Aisha Da Nana Hafsah sannan hadi da kafirta wani adadi na sahabban manzon Allah. To idan masu sauraro Sun fahinci banbance babancen to akan hakane zan gina raddi na akan rubutun da akayi.  Don haka a biyo don ...

Ya kamata a dinga tabbatar da sahihancin labari kafin a yada - Sheikh Sabi'u Jibia

Sheikh Ibrahim Sabi'u ya yi kira ga 'yan Social Media da su dinga tabbatar da Ingancin labari kafin su yada shi. Mataimakin shugaban majalissar ta kungiyar JIBWIS dake tarayyar najeriya Sheikh (Barr) Ibrahim Sabi'u Jibia, a yayin da yake gabatar da khudbar sallar juma'a yayi kira  ga masu amfani da kafafen sadarwar zamani (Social Media) su guji yada sharri da labarin karya. Ya kara da cewa: yana da kyau mutane  su dinga bincike domin tabbar da ingancin labari kafin su yada shi don gudun aikata abinda zai sa mutum ya wayi gari yana mai ladama game da abinda ya aikata. Kazalika ya karanto ayoyi daga  alqur'ani mai girma da hadisan Annabi (S.A.W) wadanda suke magana akan haramcin yin irin wannan mummunan aiki, wanda yin haka babban abin kyama ne a wajen Allah madaukakin sarki. A cewarsa tsawon lokaci da ya gabata akan samu batagarin malamai ne masu karantar da hadisan karya a yayin da suke karantar da dalibansu, amma yanzu zamani ya canza, kana kwance a gida za kai ta ...