Skip to main content

Yau shekara daya kenan da nada Sheikh Barr. Ibrahim Sabiu a matsayin "Sarkin Malaman Jibia"

Yau Lahadi 05/07/2020 Sheikh Barr. Ibrahim Sabiu ya yi shekara daya a matsayin "Sarkin Malaman Jibia".

Tarihi ya nuna cewa tun farkon kafuwar masarautar Jibiya ba'a taba bada mukamin Sarkin Malamai ba sai a shekarar data gabata, inda aka dauko daya daga cikin Malaman da ke fadi tashi don ganin addinin Muslunci  ya samu gindin zama a fadin duniyar nan. 

A shekarar data gabata ne, Mai girma Sarkin Arewan Katsina-Hakimin Jibia Alhaji Rabe Rabi'u Ibrahim, ya bada wannan mukami ga Malam Ibrahim Sabi'u, wanda akayi bikin nadin sarautar a ranar juma'a 05/07/2019 da misalin karfe 10 na safe, a fadar mai masarautar dake Jibiya.


Barrister Ibrahim Sabi'u, ya kasance dan uwa na jini ga Sarkin Arewan Katsina-Hakimin Jibia Alhaji Rabe Rabi'u Ibrahim,  wannan alaka ta nuna cewa 'ya'yan wa da kanine, Sarkin Malamai yaya ne ga Hakimin na Jibiya. 

An nada Sheikh Barr. Ibrahim Sabi'u a matsayin Sarkin Malamai ne biyo bayan kasancewarsa shararren malamin addinin muslunci mai da'awah fadin kasar najeriya da sauran kasashen ketare. 

Kuma mutum ne mai hakuri da tawakkali da tsoron Allah, mutum ne wanda baya gudun mutane kuma ya kasance mai son ganin Al'umma sunci gaba, kazalika mutum ne wanda a koda yaushe yake kokarin nuna wa mutane mahimmancin dogaro ga Allah da Addu'a, kuma aduk lokacinda zai hau mimbarin khudubar sallar juma'a baya gushewa face yaja nunawa Al'umma mahimmancin Tuba zuwa ga Allah (Istigfar) da salatin Annabi.

Malam mutum ne mai yiwa Al'umma wasilci da su kasance masu gaskiya da rikon amana aduk inda suka tsinci kansu, sannan ya kasance mai gudun duniya (Tawadhu'u) kuma mai fadawa kowa gaskiya komai rashin dadinta.

Babu shakka wannan mukami nasa na Sarkin Malamai an bayar dashi a inda ya dace,  domin ya taimaki Al'ummar musulmi ta bangarori da dama, musamman yadda malamin ya sadaukar da rayuwarsa domin kare martabar addinin muslunci da musulmai bakidaya.

Muna rokon Allah madaukakin sarki ya karawa rayuwarsa Albarka, ya albarkaci zuriyyarsa, yasa Aljanna tazam makoma a gare shi.


Muna Addu'a Allah ya kara masa lafiya da nisan kwana domin anfanuwar addinin muslunci.

Comments

Popular posts from this blog

Makarantar Sheikh Ibrahim Sabi'u Jibia ta gudanar da taro domin sanin makamar aiki

Makarantar Sheikh Ibrahim Sabi'u Jibia (MASISIJA) ta gudanar da muhimmin taro domin sanin makamar aikinta na yada da'awar maluman muslunci.  Ranar laraba 10/06/2020 wasu daga cikin jagororin wannan kungiya suka yi taro inda suka tattauna akan muhimman abubuwanda zasu taimaka masu a fagen aikinsu.  Watanni biyu da suka gabata kungiyar MASISJA ta shirya wata muhadara mai taken "Tambayoyi da Amsoshi" ta tsawon sati shidda (6) wadda Sheikh Barista Ibrahim Sabi'u Jibia ke gabatarwa.  A cikin ikon Allah,  an gabatar da ta tsawon makonni hudu (4) sai cutar Covid-19 ta billo wanda hakan yasa hukuma ta dakatar da dukkanin wani taro domin samun kariya daga cutar.  To Allah da ikonsa kuma bayan cutar ta lafa a jihar Katsina, yanzu an cigaba da harakoki kamar yadda aka saba.  Saboda haka ne kungiyar MASISJA, a karkashin wannan mitin, ta shirya tsaf domin cigaba da muhadarar tsawon sati biyu wadda mata ne kadai za ayi wa banda maza ka...

MA'ANAR SHI'A DA MANUFOFINSU (001)

Wannan raddi ne zuwa ga Ado Lamama game da shirmenda yayi a matsayin raddi zuwa ga Malamin Sunnah Alkali Sheikh Lawal Musa Jibia.  Daga: Sheikh Mustafa Mansur Jibia Da farko Inaso in fara da bayani akan minene shia.  Hakika shi'a kishiyar sunnah ce ta fuskar akida.  Sunnah tana nufin addinin da manzon Allah Ya zo dashi kuma mai yin irinsa ya yarda da sahihancin sayyidnah Abubakar, umar, Uthman da Aliyu, tareda gamsuwa da tsarkin dukkanin matayen manzon Allah, gami da yarda da cewa duk sahabbai adalai NE. To wannan shine atakaice maganar Sunnah, kuma kishiyar hakan to shine shia, kamar kudurce cewa sayyidnah Abubakar, umar da uthman mutanen banza ne kuma yan wuta, sannan matan manzon akwai na banza acikinsu, musamman Nana Aisha Da Nana Hafsah sannan hadi da kafirta wani adadi na sahabban manzon Allah. To idan masu sauraro Sun fahinci banbance babancen to akan hakane zan gina raddi na akan rubutun da akayi.  Don haka a biyo don ...

Ya kamata a dinga tabbatar da sahihancin labari kafin a yada - Sheikh Sabi'u Jibia

Sheikh Ibrahim Sabi'u ya yi kira ga 'yan Social Media da su dinga tabbatar da Ingancin labari kafin su yada shi. Mataimakin shugaban majalissar ta kungiyar JIBWIS dake tarayyar najeriya Sheikh (Barr) Ibrahim Sabi'u Jibia, a yayin da yake gabatar da khudbar sallar juma'a yayi kira  ga masu amfani da kafafen sadarwar zamani (Social Media) su guji yada sharri da labarin karya. Ya kara da cewa: yana da kyau mutane  su dinga bincike domin tabbar da ingancin labari kafin su yada shi don gudun aikata abinda zai sa mutum ya wayi gari yana mai ladama game da abinda ya aikata. Kazalika ya karanto ayoyi daga  alqur'ani mai girma da hadisan Annabi (S.A.W) wadanda suke magana akan haramcin yin irin wannan mummunan aiki, wanda yin haka babban abin kyama ne a wajen Allah madaukakin sarki. A cewarsa tsawon lokaci da ya gabata akan samu batagarin malamai ne masu karantar da hadisan karya a yayin da suke karantar da dalibansu, amma yanzu zamani ya canza, kana kwance a gida za kai ta ...